2 Oktoba 2025 - 18:57
Source: ABNA24
Isra'ila Ta Kame Jiragen Ruwa 40 Na Tawagar Sumud 

Kafofin yada labaran yahudawan sahyoniya sun rawaito cewa sojojin kasar Isra'ila sun kwace iko da jiragen ruwa sama da 40 daga cikin jiragen ruwa na ƙasa da ƙasa na Sumud.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: A cewar wadannan rahotanni, ana tura daruruwan mutanen da ke cikin jiragen ruwan zuwa tashar jiragen ruwa na Ashdod domin aikewa da su daga nan zuwa kasar.

An kuma dakatar da jirgin "Mikono", wanda ya isa ruwan Gaza a 'yan kwanakin da suka gabata.

A cewar wani wakilin gidan talabijin na Press TV, ya zuwa yanzu an kame masu fafutuka fiye da 100 daga kasashe daban-daban a cikin ayarin jiragen, kuma a yanzu ya zama wajibi gwamnatocinsu su mayar da martani kan wannan mataki na Isra'ila.

Isra'ila ta fitar da sanarwa ta hannun Ma'aikatar Harkokin Wajenta cewa: Mun dakile yunkurin "Sumud flotilla" na kutsawa cikin killacewar Gaza.

Ma'aikatar harkokin wajen Isra'ila ta yi ikirarin cewa babu wani jirgin ruwan Hamas-Sumud da ya iya shiga yankin yakin ko karya dokar hana zirga-zirgar jiragen ruwa.

An kuma sanar da cewa dukkan fasinjojin na kan hanyar zuwa yankunan da aka mamaye kuma za a kai su Turai daga can.

A karshe ma'aikatar harkokin wajen Isra'ila ta yi barazanar cewa idan jirgin na karshe ya yi yunkurin da kokarin karya shingen da aka yi masa, to shi ma za a kwace shi.

Your Comment

You are replying to: .
captcha